WAKAR DA AKAYI WA ABDULJABBAR

 Na fito gaba gaɗi

Dakta Rabe ya firgita ni


Ta taho da littafa

Sai Kabiru ya hargitsa ni


Sai na dosa kwana da wayau

Babu wanda ya tallafa ni


An ka juya gun Maɗatai

Nan da nan ko ya jijjiga ni


Har da ma Masa'udu shi ma

Bai raga ba ya ƙarasa ni


Na ji kunya an ƙure ni

Gaskiya ta ƙaryata ni


An ƙure dukkan gudu na

Na ji kaye, na yi rauni


Yanzu an san ban da hujja

Ni yawan fahari gare ni


Can cikin yaran gidana

Nai ta surutu da sai ni


Nai ta cewa koda waye

Zan buga ni ban da rauni


Yau ko an zo an ritsa ni

Ga shi nan an lallasa ni


Nai ta zare ido da wayau

Sai zufa da ta lulluɓe ni


Har na ɗau robar ruwana

Ban sani ba na sha da hauni


Sai na ce ba lokaci ne

Babu adalci gare ni


Na sani ƙarya nake yi

Duniya ta kunyata ni


An yi min zindir a titi

Video ya sajjala ni


'Yan jaridu na ta cewa

Ya akai aka jijjiga ni?


Sai na ce musu ya kuke so

Na yi bayan an ƙure ni?


Yanzu kowa ya ga cewa

An gama, an murmusa ni


Ban da hujja ba karatu

Ni biɗar girma ya kai ni


-Tammat bihamdil Lah

Asgar2021

Comments